Abba kabiru Yusuf yayi wannan furuci a shafinsa na twitter inda yake cewa'
"Kamar yadda muka kuduri aniyar dawo da tsarin birnin Kano; Ina shawartar Jama'a da su daina duk wani aikin gine-gine na filayen gwamnati a ciki da wajen makarantu, wuraren addini da na al'adu, da dukkan asibitoci, da makabarta, da kuma gefen katangar birnin jihar Kano. - AKY"
Wannan maganar ta kawo cece kuce ga masu bayyyana ra,ayinsu inda wasu ke ganin zai jawowa kansa bakin jini, daya tsaya yin rusau gwanda ya tsaya ya yaci da kano_"a inda wasu kuma suna ganin hakan a matsayin hakan ya kamata ayi.
Zaka iya bayyyana ra,yinka kaima ta comment shin da wane bangare kake tare

0 Comments